VANGUARD ta rawaito cewa wannan na kunshe ne cikin rahoton taron da ke gudana tsakanin Bankin da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) a Washington, Amurka.
Bankin Duniya ya yi duba cewa nan da 2027 talauci zai karu a Nijeriya da kashi 3.6 nan da shekaru biyar, farawa daga 2027.
Rahoton ya nuna mawuyacin hali da ƴan Nijeriya ke ciki duk da nasarorin habbakar tattalin arziki a kasar, musamman bangaren da ba na man fetur ba.
Sai dai kuma rahoton ya ce tsare-tsaren gwamnatin na gyaran tattalin arziki ya haifar da tsaiko wajen bunƙasar tattalin arziki a fadin ƙasar.
Tags:
Labarai